Super Eagles za ta kara da Zimbabwe ranar Lahadi


 



 Tawagar ƙwallon ƙafa ta Najeriya Super Eagles ta sauka a Rwanda a sanyin safiyar Asabar, domin buga wasa da Zimbabwe a neman shiga gasar cin kofin duniya da za a yi a 2026.

Najeriya za ta buga wasa na biyu a cikin rukuni na uku bayan tashi 1-1 da Lesotho ranar Alhamis.

A tsakar daren Asabar Najeriya ta yi shatar jirgin sama daga filin jirgin sama na Victor Attah zuwa Kigali.

Daga nan ne za ta shiga motar da za ta yi awa biyu zuwa Butare, inda za ta fafata a filin wasa na Huye, mai cin 'yan kallo 20,000.

Comments